SAQO ZUWA GA YAN KADUNA.. AL'UMMAR MUSULUMA JAHAR KADUNA NA FUSKANTAR MATSALA AZABEN GWAMNA WANDA ZAI GUDANA RANAR ASABAR

Alummar Musulman jahar kaduna Na fuskantar Matsala Azaban gwamna wanda zai gudana Ranar Asabar 9/3/2019 Daga Farouq Sobeka Assalafy Duk wani musulmi a ko’ina yake a duniya ba wai musulmin jihar Kaduna ba sai ya girgiza idan yaji mummunan tanadin da Kiristocin kudancin jihar Kaduna sukayi domin su tabbatar da sun kawar da Malam Nasir El-Rufai daga kan kujerar gwamnan jihar. Nayi imani da Allah zaben gwamnoni da ‘yan majalisun jiha da za’a gudanar nan da kwana 7 babu shakka Malam Nasir El-Rufai ba da ‘dan takaran gwamna na jam’iyyar PDP Alhaji Isah Ashiru kudan zaiyi takara ba, da kungiyar Kiristoci ta CAN reshen Jihar Kaduna zaiyi takara. Shi kansa Malam Nasir El-Rufai ya tabbatar da wannan, kamar yadda kwanaki ya bayyana cewa yayi imani da Allah ko shugaban kiristocin duniya (Papa Roma) zai kawo ya ajiye a matsayin mataimakinsa ya san cewa kiristocin Kaduna ba zasu zabeshi ba saboda tsananin kiyayyar da suke masa, saboda me yasa? Tsohon Gwamnan jihar Kaduna Mr Yakowa yayiw...